Iƙirarin ƙarya ya yaɗu cewa babu wanda aka taɓa kamawa ko hukuntawa saboda harin ta’addanci a Arewa
Wani mai amfani da X, Shehu Ghazali Sadiq (@shehusky), yayi iƙirarin ...
Wani mai amfani da X, Shehu Ghazali Sadiq (@shehusky), yayi iƙirarin cewa gwamnatin Nijeriya bata taɓa kamawa da hukunta wani ba akan harin ta’addanci dake faruwa a Arewacin Nijeriya ba. ...
Hukunci: ƘARYA NE
Bincike ya nuna mutane da yawa da ake zargin ‘yan ta’adda ne gwamnatin Nijeriya ta kama da kuma hukuntasu a ‘yan shekarun nan.
Fitattu a cikin wanda aka kama akwai Abubakar Dikko wanda aka fi sani da Kabiru Sakkwato, wanda ya shirya harin bam da aka kai ranar kirsimeti a Jahar Neja a 2011.
Kabiru, wanda ƙasurgumin jami’in ƙungiyar Boko Haram ne, yan sanda sun kama shi da farko ranar 1 Junairu, 2012, amma ya tsere daga komarsu bayan kwana biyu a hanyar zuwa gidansa domin gudanar da bincike a Abaji dake Babban Birnin Tarayya.
An sake kama shi a Mutum-Biu dake ƙaramar hukumar Gassol dake Jahar Taraba a Fabrairu 2012 inda aka tuhumeshi akan ta’addanci.
Babbar Kotu dake Abuja ta same shi da laifin ta’addanci kuma ta yanke masa hukuncin rai da rai a gidan yari ranar 20 Disamba, 2013.
Wata shahararriyar shari’a itace ta tsohon shugaban ƙungiyar Ansaru da suka ɓalle daga Boko Haram wato Khalid Al-Barnawi, wanda aka tuhumeshi da yin garkuwa da kuma kashe ‘yan kasashen waje 10.
Al-Barnawi wanda asalin sunan sa Usman Umar Abubakar, jami’an tsaron hadin gwiwa sun kama shi ranar 1 Afrilu, 2016 a Lokoja babban birnin Jahar Kogi.
Bayan waɗanann misalai akwai wasu da yawa da suka nuna gwanmatin Nijeriya ta hukunta ‘yan ta’adda da yawa.
A farkon shekarar 2023 ne gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari tace tayi hukunci 1,500 daya danganci ta’addanci inda tai nasara akan shari'u 397 daga watan Mayu 2015 zuwa ƙarshen mulkinsa.
Sannan a 2023 ne, Alƙalin Alƙalai mai ci kuma ministan Shari’a na ƙasa Lateef Fagbemi ya sanar da ci gaba da shari’un wanda ake zargi ‘yan Boko Haram ne dake tsare a hannun gwamnati.
Fagbemi ya ƙara da cewa gwamnatin taryya ta kama mutane 366 da laifi, sannan an saki mutane 896 saboda rashin ƙwaƙƙwarar hujja.
END CREDITS:
Rubutawa: Nurudeen Akewushola
Fassara: Ali Isa Musa
Mai ba da Labari: Musa Sunusi Ahmad
Kara koyo: https://factcheckhub.com/false-claim-circulates-that-nobody-was-arrested-prosecuted-for-terrorist-attacks-in-northern-nigeria/[+] Show More